fidelitybank

Mu na da sharuddan da za mu amince da dokokin gyaran harajin Tinubu – Shekarau

Date:

Kungiyar farfado da dimokuraɗiyyar a Arewa (LND), ta gabatar da sharuɗɗan amincewa da dokokin gyaran harajin Shugaba Tinubu.

Da yake magana a wani taron jama’a da aka gudanar a Abuja, shugaban kungiyar kuma tsohon gwamnan Kano, Sanata Ibrahim Shekarau ya jaddada muhimmancin magance matsalolin da kwamiti da aka kafa don tantance kudurorin ya gano.

A cewarsa, binciken kwamitin ya nuna cewa akwai matsalolin zamantakewa, al’adu, da na shugabanci da za su iya haifar da babbar matsala idan aka yi watsi da su.

“Kungiyar LND na kallon ƙudurorin gyaran haraji a matsayin wata dama don bunƙasa zaman lafiyar tattalin arziƙin Najeriya tare da magance matsalolin kundin tsarin mulki, al’adu, da shugabanci,” inji shi.

Ya yi kira da a yi gyare-gyare sosai kan ƙudurorin domin tabbatar da adalci, bunƙasa hadin kan ƙsa, da kuma tabbatar da rarraba albarkatu bisa gaskiya da adalci.

Ana sa ran matsayar LND da shawarwarinta za su taka muhimmiyar rawa wajen tsara tattaunawar gyaran haraji da ake yi a majalisar tarayya.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp