fidelitybank

Mu na da sharuddan da za mu amince da dokokin gyaran harajin Tinubu – Shekarau

Date:

Kungiyar farfado da dimokuraɗiyyar a Arewa (LND), ta gabatar da sharuɗɗan amincewa da dokokin gyaran harajin Shugaba Tinubu.

Da yake magana a wani taron jama’a da aka gudanar a Abuja, shugaban kungiyar kuma tsohon gwamnan Kano, Sanata Ibrahim Shekarau ya jaddada muhimmancin magance matsalolin da kwamiti da aka kafa don tantance kudurorin ya gano.

A cewarsa, binciken kwamitin ya nuna cewa akwai matsalolin zamantakewa, al’adu, da na shugabanci da za su iya haifar da babbar matsala idan aka yi watsi da su.

“Kungiyar LND na kallon ƙudurorin gyaran haraji a matsayin wata dama don bunƙasa zaman lafiyar tattalin arziƙin Najeriya tare da magance matsalolin kundin tsarin mulki, al’adu, da shugabanci,” inji shi.

Ya yi kira da a yi gyare-gyare sosai kan ƙudurorin domin tabbatar da adalci, bunƙasa hadin kan ƙsa, da kuma tabbatar da rarraba albarkatu bisa gaskiya da adalci.

Ana sa ran matsayar LND da shawarwarinta za su taka muhimmiyar rawa wajen tsara tattaunawar gyaran haraji da ake yi a majalisar tarayya.

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp