Aƙalla ma’aikata 450 ne da ke aiki a ofisoshin jakadancin Najeriya a ƙasashe 109 ba su samu albashinsu ba na wata biyar zuwa shida.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa ma’aikatan da ke ƙarƙashin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya na cikin mawuyacin hali na rashin kuɗi ta yadda wasunsu ba ko iya biyan kuɗin haya da kuɗin makarantar ‘ya’yansu ko biyan wasu muhimman buƙatun iyalinsu.
Mai riƙon muƙamin kakakin ma’aikatar, Kimiebi Ebienfa, ya ce ma’aikatar na sane da wannan hali da ma’aikatan ke ciki, ya kuma bayar da tabbacin cewa za a shawo kan matsalar.
Manyan jami’an fadar gwamnatin tarayya da kuma jami’an da ke aiki a ma’aikatar harkokin wajen Najeriya sun bayyana wa jaridar cewa ana buƙatar dala biliyan ɗaya domin biyan bashi da kuma tafiyar da harkokin ofisoshin jakadancin ƙasar daban-daban a ƙasashen duniya.
A lokacin da Shugaba Tinubu ya hau mulki ya sake nazarin manufofin waje na ƙasar inda ya dawo da jakadu 83 a watan Satumba na 2023.
Sai dai kuma matsalar rashin kuɗi ta haifar da jinkiri wajen naɗa sababbin jakadun har yanzu.
To amma jaridar ta ruwaito cewa rashjin naɗa jakadun ya ƙara haifar da jinkiri wajen biyan albashin ma’iakatan ofisoshin jakadancin na Najeriya.