fidelitybank

Mu na cikin mawuyacin hali saboda ba albashi – Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Najeriya

Date:

Aƙalla ma’aikata 450 ne da ke aiki a ofisoshin jakadancin Najeriya a ƙasashe 109 ba su samu albashinsu ba na wata biyar zuwa shida.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa ma’aikatan da ke ƙarƙashin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya na cikin mawuyacin hali na rashin kuɗi ta yadda wasunsu ba ko iya biyan kuɗin haya da kuɗin makarantar ‘ya’yansu ko biyan wasu muhimman buƙatun iyalinsu.

Mai riƙon muƙamin kakakin ma’aikatar, Kimiebi Ebienfa, ya ce ma’aikatar na sane da wannan hali da ma’aikatan ke ciki, ya kuma bayar da tabbacin cewa za a shawo kan matsalar.

Manyan jami’an fadar gwamnatin tarayya da kuma jami’an da ke aiki a ma’aikatar harkokin wajen Najeriya sun bayyana wa jaridar cewa ana buƙatar dala biliyan ɗaya domin biyan bashi da kuma tafiyar da harkokin ofisoshin jakadancin ƙasar daban-daban a ƙasashen duniya.

A lokacin da Shugaba Tinubu ya hau mulki ya sake nazarin manufofin waje na ƙasar inda ya dawo da jakadu 83 a watan Satumba na 2023.

Sai dai kuma matsalar rashin kuɗi ta haifar da jinkiri wajen naɗa sababbin jakadun har yanzu.

To amma jaridar ta ruwaito cewa rashjin naɗa jakadun ya ƙara haifar da jinkiri wajen biyan albashin ma’iakatan ofisoshin jakadancin na Najeriya.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp