fidelitybank

Mu na bukatar dala miliyan 910 don tallafawa Najeriya – UNICEF

Date:

Majalisar Dinkin Duniya ta ce, tana buƙatar dala miliyan 910 domin shawo kan matsalar jin ƙai a arewa maso gabashin Najeriya.

Hakan na zuwa ne bayan rahoton haɗin guiwa da gwamnatin tarayya da majalisar dinkin duniya suka fitar a watan Nuwanba na 2024 wanda ya nuna cewa ƙasar na fuskantar matsalar yunwa, inda mutane sama da miliyan 30 aka yi hasashen cewa za su fuskanci ƙarancin abinci a 2025.

A wajen taron ƙaddamar da kundun tsare-tsaren ayyukan jin ƙai na arewa maso gabas da ya gudana a jiya Alhamis a Abuja, MDD ta jaddada cewa “Mutane kusan miliyan takwas na buƙatar agaji a jihohin, Borno da Adamawa da Yobe, inda ke akwai mutane miliyan 2.3 da suka rasa muhallansu.

MDD ta ce rikicin da ake fuskanta a ƙasashen Ukraine da Gaza da Sudan ne suka dauke hankalin duniya daga na arewa maso gabashin Najeriya.

A cewar takardun Majalisar Dinkin Duniya, bukatar kudi da ake da ita a yanzu ya sanya matsalar jin ƙai a arewa maso gabas ta zama mafi tsada a yammaci da tsakiyar Afirka; kuma mai yiwuwa ya zarce na Chadi, Mali, Burkina Faso, da Nijar. In ji BBC.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp