Majalisar Dinkin Duniya ta ce, tana buƙatar dala miliyan 910 domin shawo kan matsalar jin ƙai a arewa maso gabashin Najeriya.
Hakan na zuwa ne bayan rahoton haɗin guiwa da gwamnatin tarayya da majalisar dinkin duniya suka fitar a watan Nuwanba na 2024 wanda ya nuna cewa ƙasar na fuskantar matsalar yunwa, inda mutane sama da miliyan 30 aka yi hasashen cewa za su fuskanci ƙarancin abinci a 2025.
A wajen taron ƙaddamar da kundun tsare-tsaren ayyukan jin ƙai na arewa maso gabas da ya gudana a jiya Alhamis a Abuja, MDD ta jaddada cewa “Mutane kusan miliyan takwas na buƙatar agaji a jihohin, Borno da Adamawa da Yobe, inda ke akwai mutane miliyan 2.3 da suka rasa muhallansu.
MDD ta ce rikicin da ake fuskanta a ƙasashen Ukraine da Gaza da Sudan ne suka dauke hankalin duniya daga na arewa maso gabashin Najeriya.
A cewar takardun Majalisar Dinkin Duniya, bukatar kudi da ake da ita a yanzu ya sanya matsalar jin ƙai a arewa maso gabas ta zama mafi tsada a yammaci da tsakiyar Afirka; kuma mai yiwuwa ya zarce na Chadi, Mali, Burkina Faso, da Nijar. In ji BBC.