fidelitybank

Mu na buƙatar addu’o’inku domin jagoranci nagari – Tinubu

Date:

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya buƙaci ƴan Najeriya su riƙa yi wa shugabanninsu addu’a, inda ya ce su ma suna buƙatar hakan tare da goyon baya domin ƙasar ta ci gaba.

Tinubu ya bayyana haka ne a saƙonsa na Kirsimeti, inda ya taya al’uumar Najeriya murna, tare da kira gare ga Kiristoci su yi amfani da ranar domin sabunta burinsu na samun ingantacciyar Najeriya.

Shugaban ya sake jajanta wa waɗanda suka rasu a turmutsutsun Oyo da Anambra da Abuja, inda ya ce shugabanni ma suna buƙatar addu’o’in domin su yi jagoranci nagari.

Ya kuma yi kira ga ƴan ƙasar su tuna marasa ƙarfi, musamman maƙwabta da ƴan’uwa da abokai da sauran abokan hulɗa.

“Shugabanni ma suna buƙatar addu’o’i da goyon baya. Idan muka samu goyon bayanku, za mu yi mulki nagari. Najeriya ta kama hanyar inganci domin alamu suna nuna cewa akwai haske a gaba.”

Ya kuma ce za su tabbatar dukkan masu tafiye-tafiye sun je inda za su je lafiya, ta hanyar tabbatar da tsaro da kuma samar da hanyoyin sufuri kyauta.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp