Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya buƙaci ƴan Najeriya su riƙa yi wa shugabanninsu addu’a, inda ya ce su ma suna buƙatar hakan tare da goyon baya domin ƙasar ta ci gaba.
Tinubu ya bayyana haka ne a saƙonsa na Kirsimeti, inda ya taya al’uumar Najeriya murna, tare da kira gare ga Kiristoci su yi amfani da ranar domin sabunta burinsu na samun ingantacciyar Najeriya.
Shugaban ya sake jajanta wa waɗanda suka rasu a turmutsutsun Oyo da Anambra da Abuja, inda ya ce shugabanni ma suna buƙatar addu’o’in domin su yi jagoranci nagari.
Ya kuma yi kira ga ƴan ƙasar su tuna marasa ƙarfi, musamman maƙwabta da ƴan’uwa da abokai da sauran abokan hulɗa.
“Shugabanni ma suna buƙatar addu’o’i da goyon baya. Idan muka samu goyon bayanku, za mu yi mulki nagari. Najeriya ta kama hanyar inganci domin alamu suna nuna cewa akwai haske a gaba.”
Ya kuma ce za su tabbatar dukkan masu tafiye-tafiye sun je inda za su je lafiya, ta hanyar tabbatar da tsaro da kuma samar da hanyoyin sufuri kyauta.