Rundunar ƴansanda ta tabbatar da mutuwar ƙarin mutum uku sakamakon turmutsitsin da aka yi a jihar Bauchi lokacin raba zakkar kuɗi.
Tun da farko hukumomi sun tabbatar da mutuwar mata huɗu.
Sai dai wani ɗanjarida a jihar ta Bauchi Hassan Mohammed wanda ke bibiyar lamarin, ya ce yana tunanin mutanen da suka mutu za su kai kusan 17.
Ƴansanda sun ce sun ƙaddamar da bincike game da turmutsitsin da ya janyo mutuwar mutanen.
A ranar Juma’a, an samu ɗaliban jami’ar jihar Nasarawa da suka mutu a irin wannan turmutsitsin na raba abinci.