Hukumar zaɓe ta ƙasa a Najeriya, Inec, ta ce tana bincike kan ƙorafin da aka kan wasu takardun rubuta sakamakon zaɓe da aka cike tun kafin fara kaɗa ƙuri’a a jihar Kogi.
“Hukumar na ɗaukar wannan lamari da muhimmanci,” in ji ta cikin wani saƙon X.
“Manyan jami’anmu da aka tura jihar na bincike game da lamarin, kuma za mu bayyana matakin da muka ɗauka nan take.”
Cikin wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, Ƙungiyar sa-ido kan zaɓuka da kyautata dimokuraɗiyya ta Yiaga Africa ta ce lamarin ya faru ne a rumfar zaɓe mai lamba PU 004, Eni Ward da ke ƙaramar hukumar Ogori/Magongo.
Ƙungiyar ta wallafa wani hoto da ake zargin na sakamakon zaɓen rumfar ne da aka riga aka cike, tana mai kira ga hukumar zaɓe ta Inec da ta bincika lamarin.
Shi ma ɗan takarar gwamnan Kogi na PDP, Sanata Dino Melaye, ya yi irin wannan zargi cikin wani bidiyo da ya wallafa.