Kamfanin rarraba wutar lantarki na Najeriya (TCN) ya ce yana aiki tukuru wajen ganin an gayra wutar lantarki a arewacin Najeriya, duk da irin kaulubale na rashin tsaro da ake fuskanta a yankin.
Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun kamfanin, Ndid Mbah ya fitar, ya ce matsalar da ake samu na rashin wutar lantarki a jihohi da dama na arewa ya faru ne sakamkon lalata layin bayar da wuta na Shiroro-Mando – wanda shi ke samar da wuta a faÉ—in yankin.
“Kalubale na rashin tsaro a yankin na janyo tsaiko wajen kammala aikin gyara layin da kuma mayar da wuta nan take,” in ji TCN.
Kamfanin ya ce ya É—auki matakin wucin gadi na amfani da layin wutar lantarki na Ugwuaji-Apir mai karfin megawatt 330 don samar da wuta, sai dai shi ma ya samu matsala.
TCN É—in ya ce yana aikin haÉ—in gwiwa da ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro domin ganin an kai ga wuraren da aka lalata layukan wuta don gyara su cikin gaggawa.
“Hakan yana da muhimmanci domin kare rayuka yayin aikin gyara layukan wutar lantarkin,” a cewar kamfanin.
Don haka ya buÆ™aci al’ummar yankin da su Æ™ara hakuri saboda suna sane da irin tasirin da rashin wutar ya janyo musamman ga rayuwar yau da kullum.