fidelitybank

Mu da Ten Hag kamar tif da taya ne – Mc Tominay

Date:

Scott McTominay ya ce, suna goyon bayan Erik ten Hag kan yadda yake gudanar da aikinsa, bayan kalubale da Manchester United ke fuskanta a bana.

Ranar Asabar ne Bournemouth ta doke United 3-0 a Old Trafford yayin karawar Premier League karo na 11 daga wasa 23 da ta yi rashin nasara a dukkan wasannin da ta buga kenan.

Ya zama wajibi United ta doke Bayern Munich, idan tana son kai wa zagaye na biyu a Champions League a kakar nan.

Bayern Munich, wadda ta kai zagaye na biyu a gasar zakarun Turai za ta ziyarci Man United mai maki hudu ta karshen teburi ranar Talata.

”Hakki ne na dukkan ‘yan wasa, shi ne kan gaba kuma mafi muhimmanci,” in ji McTominay.

”Muna da fitattun ‘yan wasa, yanzu haka muna kara kaimi don ganin mun koma kan ganiya.”

”Muna da kwararrren koci da masu taimaka masa. Muna so mu mayar da kungiyarmu kan ganiya. Wannann shi ne fatanmu.”

McTominay, mai shekara 27, ya fara buga wa Manchester United wasa a 2017 karkashin Jose Mourinho.

A makon jiya ne Ten Hag, wanda yake kakarsa ta biyu a Old Trafford, ya yi watsi da cewar rabin ‘yan wasan United ba sa tare da shi, ya ce dukkan ‘yan kwallon kansu a hade yake.

Wasu tsoffin koci-kocin United, David Moyes da Louis van Gaal da Mourinho da Ole Gunnar Solskjaer da kuma Ralf Rangnick, sun samu kansu cikin matsalar rashin jituwa da ‘yan wasa.

United tana mataki na shida a teburin Premier League kuma ta karshe a teburin Champions League, wadda ke bukatar doke Bayern Munich kafin ta kai zagayen ‘yan 16.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran Æ™asa za ka mayar da kai ba zaÉ“en 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp