fidelitybank

Motsa Jiki: Tinubu ya na da cikakkiyar lafiya – Umahi

Date:

Gwamna David Umahi na jihar Ebonyi, ya ce, Sanata Bola Ahmed Tinubu dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, yana da rai kuma ba ya bukatar ya nuna wa kowa wata hujja ta rayuwa.

Ya bayyana haka ne a safiyar yau yayin da yake gabatar da tambayoyi a Channels TV.

Ku tuna cewa an yi ta rade-radin cewa, dan takarar jam’iyyar APC na iya fuskantar wasu matsalolin rashin lafiya biyo bayan rashin halartar wata yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun siyasa suka yi.

Rahotanni sun bayyana a ranar Alhamis cewa a halin yanzu yana birnin Landan na kasar Birtaniya.

Duk da haka, Tinubu ya kuma raba bidiyo na kansa yana aiki a kan keken motsa jiki don tabbatar da cewa yana da karfi da lafiya.

Sai dai ya kasa bayyana dalilin da ya sa ba ya nan.

Da yake mayar da martani kan jita-jitar, Gwamna Umahi ya bayyana cewa mutanen da ke tambaya game da lafiyar shugabannin kasar, ciki har da na dan takarar jam’iyyarsa, na yin kadan.

“Babu wanda ke da lafiya kwata-kwata, kuma ba wanda ke rashin lafiya kwata-kwata; wannan batu daya ne. Wani batu kuma shi ne, ‘yan Nijeriya qanana ne; wasun mu kanana ne.

“Mutumin da ke motsa jiki, kun san ana yin bidiyo da yawo a kafafen sada zumunta ba tare da saninsa ba.

“Saboda haka, mutumin da ke da rai baya buĈ™atar nuna wata hujja ta rayuwa. Asiwaju yana da rai, kuma baya buĈ™atar nuna wata hujja ta rayuwa, kuma kuna iya ganin hakan.

“Ina ganin ya kamata mu mai da hankali kan abubuwan da za a iya gani saboda rayuwa kamar kasancewa cikin bas ne, kuma ba ku san inda tashar bas ta gaba take ba.

“Wasu daga cikin mutanen da ke magana kan lafiyar shugabannin kasar ba su ma san lokacin da tashar motar su ta zo ba. Don haka, ya kamata mu dogara ga abubuwan zahiri. Kowane rai da lafiya yana hannun Allah; haka nake kallo”, in ji shi.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp