fidelitybank

Motocin da basu da cikakkun takardu dole mu kama su – Kwastam

Date:

Masu shigo da motoci zuwa Najeriya, sun yi zargin cewa jami’an hukumar kwastam na kama motocin tare da cinsu tara duk da cewa an biya kudin takardu na motocin Tokumbo da ake shigo da su daga kasashen waje.

Masu motoci da direbobin matocin na zargin cewa wannan takura tafi tsanani ga motocin da ake tafiya da su yankin arewacin kasar.

Sai dai a martanin da ta mayar, hukumar kwastam, ta ce, motocin ba su da cikakkun takardu ko kuma ana shigo da su cikin kasar ba bisa ka’ida ba.

Direbobin sun yi zargin cewa jami’an hukumar na kirkiro wasu abubuwa da basu da tushe ballantana makama, inda sukan yi ikirari cewa takardun motocin basu cika ba ko kuma an biya kudi kasa da abinda ya cancanta a biya – wanda sakamakon haka kanzo a rike motocin Takumbon har sai masu motocin sun biya ko kuma a rike su.

Wannan dai a cewar direbobin, yafi tsanani musanman a kan babbar hanyar daga jihar Legas zuwa yankin arewacin kasar, duk kuwa da cewa motocin suna dauke da cikakkun takardu da biyan kuÉ—in haraji da ya cancanta a biya ga hukumar.

Dama dai gwamnati ta haramta shigo da motoci ta kan tudu wato daga iyakokin kasar da ke makwabtaka da Najeriya kamar jamhuriyar Benin da Nijar da Kamaru da kuma Chadi.

Najeriya dai kasa ce da kasuwar motocin da aka yi amfani da su a kasashen Turai da aka fi kira Tokumbo ta samu karɓuwa da kusan sama da kashi tamanin daga motocin da ke kasar Tokunbo ne. In ji BBC.

Gwamnatin kasar ta ce za a ke shigo da motoci a kasar ta gabar teku ne kadai dauke da takardu cikakku , wanda duk wani abu sabanin haka ya karya dokar kasar.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp