Masu shigo da motoci zuwa Najeriya, sun yi zargin cewa jami’an hukumar kwastam na kama motocin tare da cinsu tara duk da cewa an biya kudin takardu na motocin Tokumbo da ake shigo da su daga kasashen waje.
Masu motoci da direbobin matocin na zargin cewa wannan takura tafi tsanani ga motocin da ake tafiya da su yankin arewacin kasar.
Sai dai a martanin da ta mayar, hukumar kwastam, ta ce, motocin ba su da cikakkun takardu ko kuma ana shigo da su cikin kasar ba bisa ka’ida ba.
Direbobin sun yi zargin cewa jami’an hukumar na kirkiro wasu abubuwa da basu da tushe ballantana makama, inda sukan yi ikirari cewa takardun motocin basu cika ba ko kuma an biya kudi kasa da abinda ya cancanta a biya – wanda sakamakon haka kanzo a rike motocin Takumbon har sai masu motocin sun biya ko kuma a rike su.
Wannan dai a cewar direbobin, yafi tsanani musanman a kan babbar hanyar daga jihar Legas zuwa yankin arewacin kasar, duk kuwa da cewa motocin suna dauke da cikakkun takardu da biyan kuÉ—in haraji da ya cancanta a biya ga hukumar.
Dama dai gwamnati ta haramta shigo da motoci ta kan tudu wato daga iyakokin kasar da ke makwabtaka da Najeriya kamar jamhuriyar Benin da Nijar da Kamaru da kuma Chadi.
Najeriya dai kasa ce da kasuwar motocin da aka yi amfani da su a kasashen Turai da aka fi kira Tokumbo ta samu karɓuwa da kusan sama da kashi tamanin daga motocin da ke kasar Tokunbo ne. In ji BBC.
Gwamnatin kasar ta ce za a ke shigo da motoci a kasar ta gabar teku ne kadai dauke da takardu cikakku , wanda duk wani abu sabanin haka ya karya dokar kasar.