fidelitybank

Motoci 31 ne za su ƙwaso ƴan Najeriya daga Sudan – Gwamnati

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, manyan motoci 31 aka tanadar domin kwaso ‘yan ƙasar da suka maƙale a Sudan, don kai su Masar inda za a ɗauko su a jiragen sama zuwa Najeriya.

Babban sakatare a ma’aikatar jin-kai ta ƙasar, kuma shugaban cibiyar da ke sa ido kan halin da ‘yan ƙasar ke ciki a Sudan Dakta Nasir Sani Gwarzo ne ya bayyana haka jim kaɗan bayan wata ganawar sirri da manyan jami’an ma’aikatar a Abuja.

Ya ce an samar da manyan motocin ɗaukar fasinja 31, domin aikin kwasar ‘yar ƙasar da suka maƙale a Sudan ɗin, kuma an biya kowacce mota dala 30,000.

Ya ce jinkirin da aka samu a kan iyakar ƙasar Masar, an same shi sakamakon rashin biyan kuɗin da babban bankin ƙasar ya yi a kan lokaci, tare da buƙatar biyan kuɗin bisa da gwamnatin Masar ta yi.

Dakta Nasir Gwarzo ya ce, masu motocin sun buƙaci a biya su kuɗinsu gaba-ɗaya, duk kuwa da suna sane da cewa ba zai yiwu a tura kuɗi kai tsaye zuwa Sudan ba, dole sai da wakilai.

Ya ƙara da cewa ma’aikatar na aiki ne da hukumar tsaron farin kaya ta ƙasar da hukumar da ke tattara bayanan sirri a kan laifukan da suka shafi kuɗi ta Najeriya, wato Nigeria Financial Intelligence Unit (NFIU) wajen biyan kuɗaɗen.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp