A safiyar ranar Alhamis ne aka shiga firgita a Benin, babban birnin jihar Edo, lokacin da wata mota kirar iskar gas mai suna CNG ta fashe a tashar man NIPCO dake kan hanyar Benin zuwa Auchi.
Motar dake cikin wani faifan bidiyo tana zagayawa, ta farfasa ne yayin da mutane ke gudu don tsira da rayukansu yayin da karar fashewar ta haifar da firgici a tsakanin mazauna yankin.
An tattaro cewa mutane uku sun samu raunuka daban-daban kuma an garzaya da su wani asibiti mai zaman kansa domin kula da lafiyarsu.
Lamarin dai ya biyo bayan rashin tsaro da aka taso game da sauya motocin da ke amfani da man fetur zuwa CNG kamar yadda gwamnatin tarayya ta yi kira da a dauki matakin rage farashin sufurin bayan cire tallafin mai.