Mutum 12 sun mutu a garin ‘Ɗaki Takwas da ke ƙaramar hukumar Anka ta Jihar Zamfara, bayan sun sha wata miyar ganyen lalo mai ɗauke da sinadarin maganin kashe ‘kwari.
Mutum 25 ne da suka fito daga gidaje biyu suka sha miyar a ranar Juma’a inda tun a lokacin suka fara rasuwa ɗaya bayan ɗaya.
Yanzu haka dai akwai mutum tara daga cikinsu da ke karɓar kulawa a asibiti.
Dakta Yusuf Abubakar Haske, shi ne Daraktan Kula da Lafiyar Al’umma kuma jami’i mai Kula da cututtuka masu yaɗuwa a jihar, ya bayyana yadda al’amarin ya faru cikin tattaunawar da ya yi da BBC.
Jami’in ya tabbatar da cewa shan miyar da aka yi da ganyen lalon ce ta yi sanadiyar mutuwar mutanen.
“Manomi ne ya je ya yi feshin kwari da wasu hakukuwa da ba ya so, daga cikin hakukuwan akwai wani ganye da ake kira lalo, wanda ana miya da shi a gidajenmu na Hausa. Su kuma mutanen ba su san ya yi ba.”
“Ya yi feshin da safe, su kuma suka je da rana domin nemo ganyen da za su yi miya. Daga bisani sai suka kamu da amai da gudawa da zubar da yawu. Daga nan ne aka ɗauke su zuwa asibiti, inda ma’aikatan lafiya suka zo domin ba su taimakon gaggawa.
Jami’in lafiyan ya ce kasancewar wasu sun fi wasu shan miyar, sai ya kasance wasu sun mutu a gida yayin da wasu kuma a wani asibiti a Anka suka mutu, wasu kuma sai da aka kai su Babban Asibitin Tarayyar jihar suka mutu.
Sai dai jami’in ya ce Jihar Zamfara a shirye ta ke domin fuskantar ko-ta-kwana kan wannan lamari.