fidelitybank

Miyar ganyen Lalo ta kashe mutane 12 a jihar Zamfara

Date:

Mutum 12 sun mutu a garin ‘Ɗaki Takwas da ke ƙaramar hukumar Anka ta Jihar Zamfara, bayan sun sha wata miyar ganyen lalo mai ɗauke da sinadarin maganin kashe ‘kwari.

Mutum 25 ne da suka fito daga gidaje biyu suka sha miyar a ranar Juma’a inda tun a lokacin suka fara rasuwa ɗaya bayan ɗaya.

Yanzu haka dai akwai mutum tara daga cikinsu da ke karɓar kulawa a asibiti.

Dakta Yusuf Abubakar Haske, shi ne Daraktan Kula da Lafiyar Al’umma kuma jami’i mai Kula da cututtuka masu yaɗuwa a jihar, ya bayyana yadda al’amarin ya faru cikin tattaunawar da ya yi da BBC.

Jami’in ya tabbatar da cewa shan miyar da aka yi da ganyen lalon ce ta yi sanadiyar mutuwar mutanen.

“Manomi ne ya je ya yi feshin kwari da wasu hakukuwa da ba ya so, daga cikin hakukuwan akwai wani ganye da ake kira lalo, wanda ana miya da shi a gidajenmu na Hausa. Su kuma mutanen ba su san ya yi ba.”

“Ya yi feshin da safe, su kuma suka je da rana domin nemo ganyen da za su yi miya. Daga bisani sai suka kamu da amai da gudawa da zubar da yawu. Daga nan ne aka ɗauke su zuwa asibiti, inda ma’aikatan lafiya suka zo domin ba su taimakon gaggawa.

Jami’in lafiyan ya ce kasancewar wasu sun fi wasu shan miyar, sai ya kasance wasu sun mutu a gida yayin da wasu kuma a wani asibiti a Anka suka mutu, wasu kuma sai da aka kai su Babban Asibitin Tarayyar jihar suka mutu.

Sai dai jami’in ya ce Jihar Zamfara a shirye ta ke domin fuskantar ko-ta-kwana kan wannan lamari.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp