Ministan babban birnin tarayya, Malam Mohammed Bello, ya kira taron gaggawa na kwamitin tsaro na babban birnin tarayya Abuja, kan yadda za a samar da dabarun yaki da ta’addanci da garkuwa da mutane da fashi da makami a Abuja da kewaye.
Taron ya kuma samu halartar karamar ministar babban birnin tarayya, Dakta Ramatu Tijani-Aliyu da dukkan shugabannin hukumomin tsaro na babban birnin tarayya Abuja.
Babban mataimaki na musamman ga Ministan Tsaro na Babban Birnin Tarayya Abuja, Ambasada Habu Habu Saliu Mohammed da Kwamishinan ’Yan sandan Babban Birnin Tarayya, Babaji Sunday ne suka bayyana wa manema labarai bayan kammala taron.
Ya kara da cewa, jami’an tsaro sun kuma kuduri aniyar yin iyakacin kokarinsu don ganin an kawo karshen lamarin.
Kwamishinan ‘yan sandan ya ce, dukkan shugabannin jami’an tsaro za su sake ganawa a ofishinsa a ranar Litinin don ci gaba da dabarun abin da aka tattauna a taron gaggawar.