Ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami, ya bayyana aniyar sa ta tsayawa takarar gwamna a jihar sa a shekarar 2023.
Malami wanda ya bayyana a gaban magoya bayan sa a jihar Kebbi ya yi alkawarin ba zai ci amana su ba.
“Idan Allah cikin rahamarSa, kuma komai ya tafi daidai, ni a matsayina na dan siyasa zan tsaya takarar Gwamnan Jihar Kebbi. Ina neman goyon bayan ku.
“Ina so in sanar da cewa lallai zan tsaya takara, kuma a don haka ina dogara ga addu’o’in ku da goyon bayan ku, domin mu yi aiki tare da tsira tare. Ba ni da tarihin cin amana kuma ba zan ci amanar ku mutane ba. Zan yi muku aiki,” ya shaida wa magoya bayansa a harshen Hausa, a wani faifan bidiyo da aka gani a ranar Litinin.
A cewar jaridar Thisday, Babban Lauyan Najeriya, ya yi nuni da cewa shugabanni na bukatar mabiya kuma mabiya su kuma suna bukatar shugabanninsu domin ganin ‘yan kasa sun amfana, kamar yadda ya yi alkawarin yin aiki ba dare ba rana domin juya rayuwar ‘yan kasa.
A baya dai Malami ya shaidawa abokansa na kusa aniyarsa ta tsayawa takarar zaben jihar Kebbi.