Ministar harkokin waje ta kasar Belgium ta ce za ta ajiye aikint ana wani lokaci domin kulawa da mijinta wanda ke jinyar cutar kansar kwakwalwa.
Sophie Wilmes wadda ke rike da mukamin mataimakiyar firaministar kasar ta ce za ta dauki hutu “zuwa karshen watanni masu zafi” inda a lokacin ita da ‘yan uwanta za su sake duba halin da mijin nata ke ciki kafin ta yanke shawarar abin da za ta yi.
Cikin wata sanarwa da ya fitar, firaministan kasar Alexander De Croo ya bayyana zabin da Ms Wilmes ta yi a matsayin wanda ya kamata “kowa ya mutunta”.
Sai dai ministar ba za ta sauka daga mukamin nata ba baki daya, amma za ta mika ayyukanta ga wasu ministocin.
Ms Wilmes da mijinta Chris Stone dan asalin kasar Australia sun yi aure ne a 2009, kuma suna da ‘ya’ya uku.