Ministan harkokin cikin gida na Saudiyya Yarima Abdulaziz bin Saud bin Naif, na sa ido game yadda harkokin tsaro ke gudana yayin da mahajjata ke gudanar da tsaiwar Arfa.
A wata ganawa da ya yi da kwamandojin tsaron aikin hajjin bana a Mina, ministan ya mika sakon gaisuwar shugabannin da ke kula da Masallatai Biyu Mafiya daraja wato Sarki Salman da kuma Yarima mai jiran gado Mohammad bin Salman, ga mahajjatan bana.
Haka kuma ministan na sa-ido game da matakan da ake bi domin aiwatar tsare-tsaren da aka yi game da sha’anin tsaro a lokacin gudanar da aikin hajjin na bana. kamar yadda jaridar Saudi Gazzet ta ruwaito.