fidelitybank

Mike ya gargaɗi gwamnan Ribas a kan rikicin su da ta yi tsami

Date:

Tsohon gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike ya gargaɗin ‘yan siyasa da su riƙa martaba tsanin da ya taimaka musu wajen kai wa matsayin da suke.

Rahotonni sun ambato mista Wike – wanda a baya-bayan nan ya samu saɓani da wanda ya gaje shi a masatyin gwamnan jihar, Siminalayi Fubara – na bayyana haka a lokacin da tawagar wasu sarakunan gargajiyar jihar suka ziyarce shi a gidansa dake birnin Fatakwal.

Ministan na Abuja ya ce ya ce ”Kada ka yarda ka karya tsanin da ya taimaka maka wajen hawa inda kake, domin idan ka tashi sauko dole za ka buƙace shi, alhalin kuma baya nan”.

”Ka bar tsanin a wurin domin wasu ma za su samu su hau”, in ji shi.

Sarakunan gargajiyar waɗanda suka ziyarci tsohon gwamnan a daidai bikin zagoyawar ranar haihuwarsa, sun ce zaman lafiyar jihar shi ne babban muradinsu.

Mista Wike ya kuma tabbatar wa da sarakunan cewar shi ma a nasa ɓangare yana maraba da zaman lafiyar jihar.

A baya-bayan ne dai Mista Wike ya samu matsala da gwamnan jihar, lamarin da ya sa a cikin makon da ya gabata wasu daga cikin ‘yan majalisar dokokin jihar 27 suka fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC, wani mataki da ya sa majalisar mai ragowar mambobi biyar ta ce ta kori ‘yan majalisar 27.

Daga baya kuma gwamnan jihar ya bayar da umarnin rusa ginin majalisar, inda ya ce an yi hakan ne saboda rashin ingancin ginin.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp