Kungiyar matasan Ohanaeze ta Inyamurai (OYC) ta gargadi jam’iyyar PDP kan zaben tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar a matsayin dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023.
Shugaban kungiyar na kasa, Kwamrade Igboayaka O. Igboayaka, ya yi wannan gargadin a lokacin da yake magana a Owerri, babban birnin jihar Imo.
A cewar sa, PDP ta mika wa tsohon mataimakin shugaban kasa tikitin takarar shugabancin kasa a 2023 zai haifar da wargajewar Najeriya gaba daya.
Shugaban matasan Ohanaeze, ya kuma lura da cewa majalisar ta fusata ne kan, lokacin da Atiku Abubakar ya yi na karbar tikitin takarar shugaban kasa na PDP.
Ya ce; “Idan PDP ta ki amincewa da tikitin takarar shugaban kasa na yankin Kudu maso Gabas, abin da kawai matasan Igbo sama da miliyan 50 ya kamata su tabbatar shi ne, su ci gaba da rike Najeriya daya ta hanyar zabar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC daga yankin Kudu maso Gabas, kuma babu wani ofishi/tuta na PDP daga matakin unguwanni har zuwa jiha da za a kafa a yankin Kudu maso Gabas. Za mu yi yaki da PDP kamar yadda Yakubu Gowon ya yi domin a mayar da Najeriya kasa daya.”
A cewar majalisar, “Ya kamata Atiku Abubakar ya bi tarihin kafa PDP daga G34 karkashin jagorancin Dr. Alex Ekwueme kafin ta zama jam’iyyar siyasa, domin tabbatar da cewa, yankin Kudu maso Gabas ya fi kowace shiyya a Najeriya.”