fidelitybank

Mika wa Atiku tikitin takarar shugabancin kasa zai haifar da wargajewar Najeriya – Ƙungiyar Inyamurai

Date:

Kungiyar matasan Ohanaeze ta Inyamurai (OYC) ta gargadi jam’iyyar PDP kan zaben tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar a matsayin dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023.

Shugaban kungiyar na kasa, Kwamrade Igboayaka O. Igboayaka, ya yi wannan gargadin a lokacin da yake magana a Owerri, babban birnin jihar Imo.

A cewar sa, PDP ta mika wa tsohon mataimakin shugaban kasa tikitin takarar shugabancin kasa a 2023 zai haifar da wargajewar Najeriya gaba daya.

Shugaban matasan Ohanaeze, ya kuma lura da cewa majalisar ta fusata ne kan, lokacin da Atiku Abubakar ya yi na karbar tikitin takarar shugaban kasa na PDP.

Ya ce; “Idan PDP ta ki amincewa da tikitin takarar shugaban kasa na yankin Kudu maso Gabas, abin da kawai matasan Igbo sama da miliyan 50 ya kamata su tabbatar shi ne, su ci gaba da rike Najeriya daya ta hanyar zabar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC daga yankin Kudu maso Gabas, kuma babu wani ofishi/tuta na PDP daga matakin unguwanni har zuwa jiha da za a kafa a yankin Kudu maso Gabas. Za mu yi yaki da PDP kamar yadda Yakubu Gowon ya yi domin a mayar da Najeriya kasa daya.”

A cewar majalisar, “Ya kamata Atiku Abubakar ya bi tarihin kafa PDP daga G34 karkashin jagorancin Dr. Alex Ekwueme kafin ta zama jam’iyyar siyasa, domin tabbatar da cewa, yankin Kudu maso Gabas ya fi kowace shiyya a Najeriya.”

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp