Uwargidan shugaban kasa Remi Tinubu, ta ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta mayar da hankali a kan gyara matsalolin Najeriya, inda ta amsa cewa mijinta ba matsafi ba ne.
Ta bayyana haka ne lokacin da ta halarci addu’o’in coci a wani bangare na bikin cikar Najeriya shekara 63 da samun ‘yancin kai.
Remi Tinubu ta ce gwamnatin mijinta ta gaji dumbin matsaloli. Amma ta nanata cewa gwamnatin Tinubu ta zo da niyyar gyara matsalolin da ke damun Najeriya.
“Ba mu zo nan, don mu yi ta dora laifi a kan wata gwamnati ba, sai don gyara barnar da aka yi,” ta fada a babbar cocin kasar da ke Abuja ranar Lahadi.
“Mijina ba mai siddabaru ba ne. Zai tsaya tsayin daka ya yi aiki – kuma na yi imani sannan ina fatan cewa za ku yi amanna da wannan gwamnati.
Mafi kyawun alherai suna nan tafe gare ku,” uwargidan shugaban kasar ta ce.