fidelitybank

Messi na daf da komawa kasar Amurka da taka leda

Date:

Lionel Messi zai koma taka leda ƙungiyar ƙwallon ƙafar Amurka ta Inter Miami, bayan ya bar Paris St-Germain a kakar nan.

Tsohon ɗan wasan Barcelona na daf da ƙin amincewa da ƙunshin kwantiragin da Al Hilal ta Saudi Arabi ke shirin gabatar masa.

Yarjejeniyar Miami ta ƙunshi cewa ɗan wasan zai yi haɗakar aikin tallace-tallace da Adidas da kuma Apple.

Messi, mai shekara 35, ya lashe kyautar gwarzon ɗan kwallon duniya karo bakwai, kuma ana sa ran shi ne zai sake lashewa a bana, bayan da ya ci kofin duniya.

Wannan ne karon farko da kyaftin din Argentina zai taka leda a wajen nahiyar Turai.

Ya so ya ci gaba da wasa a Turai karin kaka daya, sai dai bai samu wani tayi mai tsoka daga wata kungiyar nahiar ba, wanda zabi ya rage masa ko dai ya koma Inter Miami ta Amurka ko kuma Al- Hilal ta Saudi Arabia.

An yi ta alakanta shi da zai koma Saudi Arabia, inda Cristiano Ronaldo ke murza leda, gasar da Karim Benzema zai fara buga wa, bayan barin Real Madrid.

To sai dai Messi ya zabi ya je ya buga gasar kwallon kafa ta Amurka a Inter Miami, sakamakon salon rayuwa da kwantiragin da ta kunshi manyan kamfanoni, bayan kwallon kafa.

Tsohon kyaftin din Argentina yana da gida a Amurka, wanda ya bayar da shi haya.

Messi ya so ya sake koma wa Barcelona, amma dokar kashe kudi daidai samu da ake kira Financial Play ba za ta bari ya koma Sifaniya ba.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp