fidelitybank

Mele Kyari na tsaka mai wuya a kan matatar Dangote

Date:

Majalisar Wakilai ta ce za ta yi kira da a kori babban jami’in kamfanin mai na Najeriya National Petroleum Company Limited, NNPC, Mele Kyari, idan har abin da suka bayyana a matsayin “yunkurin lalata matatar dangote” bai tsaya nan take ba.

Mataimakin kakakin majalisar, Philip Agbese ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja ranar Asabar.

Agbese ya bayyana cewa tuni ‘yan majalisar suka bukaci a kori shugabannin hukumar kula da harkokin man fetur ta Najeriya NMDPRA.

Ya lura cewa duka hukumomin biyu – NNPCPL da NMDPRA – sun nuna cewa suna da sha’awar lalata matatar Dangote.

Ya bayyana cewa ‘yan Najeriya da dama sun janye zanga-zangar wahala da ake shirin yi, sai dai ya kara da cewa suna son ganin an kori Kyari idan hakan zai tabbatar da tafiyar da kasar cikin sauki.

A cewarsa, majalisar za ta binciki rikicin da ke faruwa tsakanin matatar Dangote da hukumar NMDPRA.

Agbese ya ce binciken ya yi daidai da kudurin majalisar na kare dukkan kadarorin kasa da muhimman ababen more rayuwa na tattalin arziki, kamar matatar Dangote.

Ya ce: “Mun dade muna gani ta hanyar yin kamfen don bata sunan matatar man Dangote da kuma la’akari da mummunan tasirin da hakan ya haifar da firgici a kasar.

“A rubuce ne cewa majalisar ta umarci shugaban kasa ya kori shugaban NMDPRA.

“Majalisar wakilai ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen yin kira da a kori Mele Kyari, idan har yunkurin lalata matatar man, wani kadarorin kasa, bai tsaya nan take ba.”

Idan ba a manta ba tun da farko kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas ya jagoranci tawagar majalisar zuwa kamfanin matatar man dangote da ke Legas.

Abbas ya ce ziyarar ta ba da bayanai masu ma’ana da za su jagoranci matakan majalisar da kuma yanke shawara.

Ya ce majalisar na kokarin samar da yanayi mai dacewa da kasuwanci don sanya Najeriya ta zama makoma ga masu zuba jari na ciki da waje.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp