Majalisar Wakilai ta ce za ta yi kira da a kori babban jami’in kamfanin mai na Najeriya National Petroleum Company Limited, NNPC, Mele Kyari, idan har abin da suka bayyana a matsayin “yunkurin lalata matatar dangote” bai tsaya nan take ba.
Mataimakin kakakin majalisar, Philip Agbese ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja ranar Asabar.
Agbese ya bayyana cewa tuni ‘yan majalisar suka bukaci a kori shugabannin hukumar kula da harkokin man fetur ta Najeriya NMDPRA.
Ya lura cewa duka hukumomin biyu – NNPCPL da NMDPRA – sun nuna cewa suna da sha’awar lalata matatar Dangote.
Ya bayyana cewa ‘yan Najeriya da dama sun janye zanga-zangar wahala da ake shirin yi, sai dai ya kara da cewa suna son ganin an kori Kyari idan hakan zai tabbatar da tafiyar da kasar cikin sauki.
A cewarsa, majalisar za ta binciki rikicin da ke faruwa tsakanin matatar Dangote da hukumar NMDPRA.
Agbese ya ce binciken ya yi daidai da kudurin majalisar na kare dukkan kadarorin kasa da muhimman ababen more rayuwa na tattalin arziki, kamar matatar Dangote.
Ya ce: “Mun dade muna gani ta hanyar yin kamfen don bata sunan matatar man Dangote da kuma la’akari da mummunan tasirin da hakan ya haifar da firgici a kasar.
“A rubuce ne cewa majalisar ta umarci shugaban kasa ya kori shugaban NMDPRA.
“Majalisar wakilai ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen yin kira da a kori Mele Kyari, idan har yunkurin lalata matatar man, wani kadarorin kasa, bai tsaya nan take ba.”
Idan ba a manta ba tun da farko kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas ya jagoranci tawagar majalisar zuwa kamfanin matatar man dangote da ke Legas.
Abbas ya ce ziyarar ta ba da bayanai masu ma’ana da za su jagoranci matakan majalisar da kuma yanke shawara.
Ya ce majalisar na kokarin samar da yanayi mai dacewa da kasuwanci don sanya Najeriya ta zama makoma ga masu zuba jari na ciki da waje.