Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya haramta wa kungiyoyi masu aikin jin-kai bayar da agajin abinci ko wasu kayayyaki ga ’yan gudun hijirar a jihar.
Gwamna Babagana Zulum ya bayyana hakan ne a wata wasika da ya aike wa kungiyoyin ta hannun Ofishin kula da ayyukan jin-kai na Majalisar Dinkin Duniya.
Wasikar ta bukaci masu aikin agajin da su mayar da hankali wajen bunkasa harkokin dogaro da kai tare da rufe bayar da tallafin kayan abinci.
Gwamnati ta kuduri aniyar rufe dukkan sansanonin ’yan gudun hijira da aka kafa a hukumance a Maiduguri a watan Disamba.
Gwamnan ya kara da cewa shirin rufe sansanonin ’yan gudun hijirar ya kunshi taimaka wa jama’a su tsaya da kafafunsu.
Zuwa yanzu dai Gwamnatin Jihar ta Borno ta rufe sansanonin ‘yan gudun hijira guda hudu a Maiduguri, ta kuma sake tsugunar da mutanen da ke wuraren a garuruwansu na asali. A cewar Aminiya.