Majalisar Dinkin Duniya da Kungiyar Bunƙsa Tattalin Arzikin Ƙasashen Afirka ta Yamma ECOWAS, sun gargaɗi Najeriya kan batun haddasa rikici a zaɓen 2023.
Sun bayyana hakane a wani taron tattaunawa da kungiyar shiga tsakani na jam’iyyu da masu ruwa da tsaki da suka fito daga yankin arewa ta tsakiya da arewa maso gabas kan kaucewa tada fitina a Jos, babban birnin jihar Filato a ranar Talata.
MDD ta ce muddin ba a ɗauki mataki ba, za a iya samun rashin zaman lafiya a faɗin yankin.
Ita ma ECOWAS ta ce idan rikici ya ɓarke a Najeriya, babu wata ƙasa a yankin sahara da za ta iya bai wa ‘yan gudun hijirar ƙasar mafaka saboda yawansu.
Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa sama da mutane 30 ne aka ruwaito mutuwarsu yayin da da yawa suka jikkata a rikice-rikice gabanin zaɓen 2023 a sassan daban-daban na Najeriya.
An kuma kai wa ofisoshin hukumar zaɓe mai zaman kanta hare-hare a wasu sassa na Najeriya musamman ma kudu maso gabas, inda ake zargin kungiyar ‘yan awaren Biafra da kai hare-haren wanda ya yi sanadiyyar rasuwar jami’an INEC da kuma jami’an tsaro da dama.