fidelitybank

Mbappe bai rattaba sabon kwantiragi ba a PSG – Mahaifiyarsa

Date:

Mahaifiyar fitaccen dan wasan kwallon kafa Kylian Mbappe na Faransa ta karyata wani rahoto da ke cewa dan nata ya amince ya tsawaita zamansa a kungiyar Paris St. Germain da karin wasu shekaru uku, kuma ya fasa komawa kungiyar Real Madrid.

Talabijin din Channels ta rawaito cewa, Jaridar Le Parisien na cewa, masu kungiyar PSG – wato attajirai ‘yan kasar Qatar – sun yi wa Mbappe tayin albashin euro miliyan 50 a kowace kakar wasa da kuma wani alawus na euro miliyan 100 idan ya amince ya yi zamansa a kungiyar.

Sai dai mahaifiyar Mbappe, Fayza Lamari ta wallafa wani sakon Tiwita, wanda a ciki ta ce ba a kulla wata yarjejniya ba da dan nata:

“Ba a kulla yarjejeniya ba da Paris St. Germain (kuma ba a kulla ta da wata kungiyar ba)”, ta kuma ce “ana can ana tattaunawa kan makomar Kylian, saboda haka nake rokon ku da ku ba shi damar yanke hukuncin da ya dace da shi.”

Kylian ya dade yana bayyana sha’awarsa ta komawa kungiyar Real Madrid nan gaba, kungiyar da a wannan makon ta kai wasan karshe na gasar Zakarun Turai, kwanaki kadan bayan ta lashe gasar lig ta Sfaniya na 35 a tarihinta.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp