fidelitybank

Mbappe bai rattaba sabon kwantiragi ba a PSG – Mahaifiyarsa

Date:

Mahaifiyar fitaccen dan wasan kwallon kafa Kylian Mbappe na Faransa ta karyata wani rahoto da ke cewa dan nata ya amince ya tsawaita zamansa a kungiyar Paris St. Germain da karin wasu shekaru uku, kuma ya fasa komawa kungiyar Real Madrid.

Talabijin din Channels ta rawaito cewa, Jaridar Le Parisien na cewa, masu kungiyar PSG – wato attajirai ‘yan kasar Qatar – sun yi wa Mbappe tayin albashin euro miliyan 50 a kowace kakar wasa da kuma wani alawus na euro miliyan 100 idan ya amince ya yi zamansa a kungiyar.

Sai dai mahaifiyar Mbappe, Fayza Lamari ta wallafa wani sakon Tiwita, wanda a ciki ta ce ba a kulla wata yarjejniya ba da dan nata:

“Ba a kulla yarjejeniya ba da Paris St. Germain (kuma ba a kulla ta da wata kungiyar ba)”, ta kuma ce “ana can ana tattaunawa kan makomar Kylian, saboda haka nake rokon ku da ku ba shi damar yanke hukuncin da ya dace da shi.”

Kylian ya dade yana bayyana sha’awarsa ta komawa kungiyar Real Madrid nan gaba, kungiyar da a wannan makon ta kai wasan karshe na gasar Zakarun Turai, kwanaki kadan bayan ta lashe gasar lig ta Sfaniya na 35 a tarihinta.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla ÆŠanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An É—age jana’izar Aminu ÆŠantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da É—age jana'izar fitaccen É—ankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp