fidelitybank

Maƙiya ne ke kokarin lalata alaƙar Ganduje da Tinubu – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnatin Jihar Kano, ta gargaɗi al’umma game da yunƙurin wasu da ta kira “mamugunta” kuma “‘yan haɗama” da ke yaɗa wani sautin kiran waya da aka ce na Gwamna Umar Ganduje ne da kuma Ibrahim Masari.

Tun ranar Alhamis sautin muryar, wanda gwamnatin Kano ta ce “ƙirƙirarsa aka yi”, ya karaɗe shafukan zumunta, inda aka ji mutanen biyu na tattaunawa game da alaƙar Ganduje na jam’iyyar APC da Zaɓaɓɓen Shugaban Najeriya Bola Tinubu.

Suna magane kan ganawar da Tinubun ya yi da jagoran jam’iyyar adawa ta NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, a birnin Paris na Faransa cikin makon da ya gabata.

Cikin wata sanarwa da Kwamashinan Yaɗa Labarai na Kano Muhammad Garba ya fitar, gwamnatin ta ce “wasu ne da aka biya ke yunƙurin ɓata alaƙa tsakanin Ganduje da Tinubu”.

Ya ce: ” A bayyane take cewa wasu ne da ba sa son ganin daɗaɗɗiyar alaƙa tsakanin Ganduje da Tinubu, da kuma Masari ke amfani da wannan damar don cimma muradansu.

“Ba za mu bari wasu ‘yan haɗama su lalata haɗin kai tsakanin Tunubu da Ganduje ba.”

A ranar 29 ga watan Mayu za a rantsar da Bola Tinubu a matsayin shugaban Najeriya na 16 bayan ya yi nasara a zaɓen watan Fabarairu. Sai dai jam’iyyun adawa na ƙalubalantar sakamakon zaɓen a kotu.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp