Wasu daga cikin al’umma a Maiduguri babban birnin jihar Borno, sun tashi da murnar, bayan dawowar wutar lantarki da a ka yi musu a yankunan su.
Tun cikin watanni 11 bayan katsewar wutar lantarki, lamarin da ya biyo bayan lalata kayayyakin aiki da manyan layukan wutar lantarki a birnin da ‘yan Boko Haram su ka yi.
Lamarin dai ya gurgunta masu kananan sana’o’i tare da tilastawa mutane yin amfani da injin janareta a matsayin madadinsu.
An fara dawo da wutar lantarki a yankin Bulunkutu a ranar 22 ga watan Disamba sannan kuma a unguwar Pompamari dake cikin birnin.
Mazauna yankin musamman matasa masu kananan sana’o’i kamar cajin waya da bushewar da sana’o’i musamman a kasuwar waya ta Jagwal da kuma mata masu sayar da kayan sanyi da bulo na kankara da masu rijiyoyin burtsatse da kananan yara na daga cikin mutanen, wanda su ka nuna murna da dawowar wutar lantarki.
Gwamnatin jihar Borno ta shiga tsakani tare da goyon bayan shirin dawo da wutar lantarki a Maiduguri, musamman a kokarin da a ke na sake hada sabbin gine-gine da layukan wutar lantarki daga Damaturu, babban birnin jihar Yobe.
Rahotanni na cewa maharan na ci gaba da lalata wasu wuraren kamar igiyoyi, lamarin da ya kawo jinkirin dawo da cikakken wutar lantarki a tsakiyar birnin.
Wani mazaunin Bulunkutu Kasuwa, Ibrahim Ali, ya shaida wa wakilinmu cewa, dawo da wutar lantarkin ya haifar da farin ciki a Bulunkutu a tsakanin masu sana’a da ‘yan kasuwa da masu injinan nika.
Ya ce, “Mun samu kiran waya da dama, domin tabbatar da ganin an dawo da hasken. Na tuna cewa wasu abokaina sun kira waya domin tabbatar da ko gaskiya ne cewa an dawo da haske. Ya zo kamar bakon labara, amma muna matukar godiya da dawowar haske a yankinmu. Mun yi imanin cewa da yawa za su koma ƙananan sana’o’insu kuma rayuwa za ta sami kwanciyar hankali sosai”. In ji Ibrahim.
Wani ma’aikacin kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Yola (YEDC) da bai so a bayyana sunansa ba, ya bayyana cewa, yawancin taransfoma da ke cikin birnin sun cire wayoyin wutar da DisCo su ka saka, domin adanawa.