fidelitybank

Mazauna Maiduguri na murnar dawowar wutar lantarki bayan shafe wata 11

Date:

Wasu daga cikin al’umma a Maiduguri babban birnin jihar Borno, sun tashi da murnar, bayan dawowar wutar lantarki da a ka yi musu a yankunan su.

Tun cikin watanni 11 bayan katsewar wutar lantarki, lamarin da ya biyo bayan lalata kayayyakin aiki da manyan layukan wutar lantarki a birnin da ‘yan Boko Haram su ka yi.

Lamarin dai ya gurgunta masu kananan sana’o’i tare da tilastawa mutane yin amfani da injin janareta a matsayin madadinsu.

An fara dawo da wutar lantarki a yankin Bulunkutu a ranar 22 ga watan Disamba sannan kuma a unguwar Pompamari dake cikin birnin.

Mazauna yankin musamman matasa masu kananan sana’o’i kamar cajin waya da bushewar da sana’o’i musamman a kasuwar waya ta Jagwal da kuma mata masu sayar da kayan sanyi da bulo na kankara da masu rijiyoyin burtsatse da kananan yara na daga cikin mutanen, wanda su ka nuna murna da dawowar wutar lantarki.

Gwamnatin jihar Borno ta shiga tsakani tare da goyon bayan shirin dawo da wutar lantarki a Maiduguri, musamman a kokarin da a ke na sake hada sabbin gine-gine da layukan wutar lantarki daga Damaturu, babban birnin jihar Yobe.

Rahotanni na cewa maharan na ci gaba da lalata wasu wuraren kamar igiyoyi, lamarin da ya kawo jinkirin dawo da cikakken wutar lantarki a tsakiyar birnin.

Wani mazaunin Bulunkutu Kasuwa, Ibrahim Ali, ya shaida wa wakilinmu cewa, dawo da wutar lantarkin ya haifar da farin ciki a Bulunkutu a tsakanin masu sana’a da ‘yan kasuwa da masu injinan nika.

Ya ce, “Mun samu kiran waya da dama, domin tabbatar da ganin an dawo da hasken. Na tuna cewa wasu abokaina sun kira waya domin tabbatar da ko gaskiya ne cewa an dawo da haske. Ya zo kamar bakon labara, amma muna matukar godiya da dawowar haske a yankinmu. Mun yi imanin cewa da yawa za su koma ƙananan sana’o’insu kuma rayuwa za ta sami kwanciyar hankali sosai”. In ji Ibrahim.

Wani ma’aikacin kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Yola (YEDC) da bai so a bayyana sunansa ba, ya bayyana cewa, yawancin taransfoma da ke cikin birnin sun cire wayoyin wutar da DisCo su ka saka, domin adanawa.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp