fidelitybank

Mazauna Libya sun yi zanga-zanga a kan ambaliyar ruwa

Date:

Daruruwan mazauna birnin Derna da ke gabashin Libya a ranar Litinin sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da hukumomin yankin, fiye da mako guda bayan ambaliyar ruwa ta kashe dubban mutane a birnin.

Masu zanga-zangar sun soki shugaban majalisar dokokin gabashin ƙasar, Aguila Saleh, da hukumomin, inda suka dora alhakin ambaliyar da ta kashe kusan mutum 4,000, a cewar alƙaluman Majalisar Dinkin Duniya.

A cikin wata sanarwa ta hadin gwiwa, masu zanga-zangar sun ce suna son a gaggauta gudanar da bincike kan ambaliyar ruwan da kuma daukar matakin shari’a kan shugabannin da ke da hannu.

Sun kuma buƙaci a biya su diyya da sake gina Derna.

Masana sun kuma bayyana cewa rashin kula da madatsun ruwa na birnin da hukumomi suka yi ne ya sa suka fashe tare da fitar da ruwa.

Masu zanga-zangar sun kuma kona gidan magajin garin Derna, Abdulmenam al-Ghaithi.

Tuni dai Firaministan Libiya Osama Hammad ya dakatar da Mista Ghaithi tare da wasu jami’an karamar hukumar Derna.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp