Dubban masu zanga-zanga a Birtaniya sun taru a tsakiyar birnin Landan domin nuna goyon bayansu ga Falasɗinawan.
Masu shirya zanga-zangar – da aka yi wa laƙabi da “Nuna goyon baya ga Falasɗinawa’ – sun yi kiran gaggauta dakatar da wuta a Gaza, tare da bayar da damar aikewa da cikakken agaji ga masu buƙata
Masu zanga-zangar riƙe da tutar Falasɗinawa sun yi ta rera waƙoƙin “A bai wa Falasɗinawan ‘yanci”.
Dubban mutanen sun cika wasu titunan birnin ciki har da titin da ke kai wa fadar firaministan ƙasar.
A ranar Juma’a ma an gudanar da irin wannan zanga-zanga a wasu ƙasashen duniya irin su Thailand da Australiya da Netherlands da Afirka ta Kudu da wasu ƙasashen Larabawa masu yawa.