fidelitybank

Mazauna Kudu ku gaggauta bayyana masu yin kisa – Buhari

Date:

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya nemi shugabanni da mazauna yankin kudu maso gabashin ƙasar da su bayyana waɗanda ke kashe baƙi da jami’an tsaro a yankin “idan sun san inda suke”.

Kiran shugaban na zuwa ne kwana ɗaya bayan wasu ‘yan bindiga sun kashe ‘yan sanda huɗu ranar Asabar da kuma kisan fararen hula shida a farkon mako a Jihar Imo.

Rundunar ‘yan sandan ƙasar ta ce mayaƙan ƙungiyar IPOB ne suka kai harin kan jami’anta a ofishinsu da ke Agwa na Jihar ta Imo.

Buhari ya kira kisan a matsayin “na ta’addanci” sannan ya nemi shugabannin yankin da “su dinga nuna ƙyamar kashe-kashen a fili don tsare al’adu da addinin mutane”.

“Waɗanda suka san mutanen da suka aikata hakan su bayyana su,” in ji shi cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasa Garba Shehu ya fitar ranar Asabar.

Shugaban ya kuma yi alƙwarin gudanar da bincike “na gaggawa” don gano “waɗanda suka aikata ta’addanci”.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp