Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya nemi shugabanni da mazauna yankin kudu maso gabashin ƙasar da su bayyana waɗanda ke kashe baƙi da jami’an tsaro a yankin “idan sun san inda suke”.
Kiran shugaban na zuwa ne kwana ɗaya bayan wasu ‘yan bindiga sun kashe ‘yan sanda huɗu ranar Asabar da kuma kisan fararen hula shida a farkon mako a Jihar Imo.
Rundunar ‘yan sandan ƙasar ta ce mayaƙan ƙungiyar IPOB ne suka kai harin kan jami’anta a ofishinsu da ke Agwa na Jihar ta Imo.
Buhari ya kira kisan a matsayin “na ta’addanci” sannan ya nemi shugabannin yankin da “su dinga nuna ƙyamar kashe-kashen a fili don tsare al’adu da addinin mutane”.
“Waɗanda suka san mutanen da suka aikata hakan su bayyana su,” in ji shi cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasa Garba Shehu ya fitar ranar Asabar.
Shugaban ya kuma yi alƙwarin gudanar da bincike “na gaggawa” don gano “waɗanda suka aikata ta’addanci”.