Ƙasashen Faransa da Netherlands sun bai wa jama’arsu shawara da su fice daga Iran sakamakon yiwuwar tsare su ba bisa ƙa’ida ba.
Kiran na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da gudanar da jerin zanga-zangar nuna ƙin jinin gwamnati a Tehran, babban birnin ƙasar.
An tsare wasu ƴan Faransa biyu tun a watan Mayu, inda a ranar Alhamis suka amsa cewa su ƴan leƙen asiri ne da ke tattara bayanai a gidan talabijin ɗin ƙasar.
An shafe kimanin mako uku ana zanga-zanga a fadin Iran bayan wata matashiya ta rasu a hannun ƴan sanda.
Sai dai hukumomin na Iran sun alaƙanta rasuwar matar da rashin lafiya mai tsawo wadda dama can ta daɗe tana fama da ita a rayuwarta, inda suka ce ba wai dukanta aka yi a ka ba kamar yadda ake ta yayatawa.