fidelitybank

Mayakan ISWAP ta sake kai sabon hari a yankin Borno

Date:

Mayakan kungiyar ISWAP, wadda ake kira da Jamā’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād, ta kai farmaki a garin Auno, a wani kauye dake karamar hukumar Konduga a jihar Borno.

Rahotanni ya nuna cewa, maharan sun afkawa al’ummar garin da safiyar ranar litinin, wanda suka rika harba manyan bindigogi.

Lamarin da ya tilastawa mutane bazama, domin tsira da rayukansu tare da kasancewa a cikin gida, yayin da ake ci gaba da harbe-harbe kamar yadda wani soja ya shaida hakan.

Ya kara da cewa,”Sojojin sun yi galaba a kan ‘yan ta’addan ne a wani artabu da suka yi da su, wanda hakan ya sa suka tsere. Ba yanzu ba a iya tantancewa ba ko akwai wadanda suka jikkata. Ba zan iya cewa watakila an sace wani ba, harin ne da aka kai kan matafiya da ke bin babbar hanya a cikin al’umma,” inji majiyar.

Tun bayan rasuwar shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau, kungiyar ISWAP ke kara karfafa gwuiwa a yankunan da ke kusa da tafkin Chadi.

Kwanan nan, ta nada Wali Sani Shuwaram, mai shekaru 45 a matsayin sabon Shugaban (Wali) na ISWAP a tafkin Chadi.

Mambobin kungiyar sun janye sauran daruruwan mayakan kungiyar Boko Haram na karkashin Shekau.

Rundunar sojin Najeriya ta sha yin ikirarin cewa an yi galaba a kan ‘yan ta’addan kuma a lokuta da yawa suna yin watsi da duk wani asarar da aka yi.

Kungiyar ta’addanci ta yi sanadin mutuwar sama da mutane 50,000 tare da raba miliyoyin mutane daga muhallansu, musamman a jihohin Adamawa da Borno da kuma Yobe.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp