Mayakan kungiyar ISWAP, wadda ake kira da Jamā’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād, ta kai farmaki a garin Auno, a wani kauye dake karamar hukumar Konduga a jihar Borno.
Rahotanni ya nuna cewa, maharan sun afkawa al’ummar garin da safiyar ranar litinin, wanda suka rika harba manyan bindigogi.
Lamarin da ya tilastawa mutane bazama, domin tsira da rayukansu tare da kasancewa a cikin gida, yayin da ake ci gaba da harbe-harbe kamar yadda wani soja ya shaida hakan.
Ya kara da cewa,”Sojojin sun yi galaba a kan ‘yan ta’addan ne a wani artabu da suka yi da su, wanda hakan ya sa suka tsere. Ba yanzu ba a iya tantancewa ba ko akwai wadanda suka jikkata. Ba zan iya cewa watakila an sace wani ba, harin ne da aka kai kan matafiya da ke bin babbar hanya a cikin al’umma,” inji majiyar.
Tun bayan rasuwar shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau, kungiyar ISWAP ke kara karfafa gwuiwa a yankunan da ke kusa da tafkin Chadi.
Kwanan nan, ta nada Wali Sani Shuwaram, mai shekaru 45 a matsayin sabon Shugaban (Wali) na ISWAP a tafkin Chadi.
Mambobin kungiyar sun janye sauran daruruwan mayakan kungiyar Boko Haram na karkashin Shekau.
Rundunar sojin Najeriya ta sha yin ikirarin cewa an yi galaba a kan ‘yan ta’addan kuma a lokuta da yawa suna yin watsi da duk wani asarar da aka yi.
Kungiyar ta’addanci ta yi sanadin mutuwar sama da mutane 50,000 tare da raba miliyoyin mutane daga muhallansu, musamman a jihohin Adamawa da Borno da kuma Yobe.