Mayakan kungiyar ta’addanci ta ISWAP sun kashe akalla mutane takwas a wani hari da suka kai karamar hukumar Biu ta jihar Borno.
Jaridar The Cable ta rahoto cewa mayakan sun farmaki kauyukan Mandaragirau da Ghuma da ke karamar hukumar a daren ranar Asabar, 26 ga watan Fabrairu, inda suka kashe mazauna takwas da kuma jikkata wasu.
Bayanai na cewa, wasu majiyoyi na rundunar soji ta dakile wani hari da ISWAP suka kai hanyar Mandaragarau a safiyar Asabar.
Rundunar sojin Najeriya, karkashin Operation Desert Sanity, da ke sintiri mai dogon zango a yankin, sun datse sadarwar ‘yan ta’addan da ke aikin dasa bama-bamai a kan hanyoyin tare da kai farmaki kan sansanin sojoji.
Amma sai dakarun suka farmaki wajen sannan suka yi maganin da yan ta’addan. Biyo bayan datsewar, sai yan ta’adda tara kan babura uku suka farmaki kauyukan Mandaragirau da Ghuma, inda suka zargi mazauna kauyukan da yiwa sojoji kwarmaton shirinsu. Rahoton ya kara da cewar maharan sun kuma kona wasu shaguna, suka sace kayan abinci da dabbobin mazauna garuruwan