Mazauna yankin Gamboru-Ngala da ke kan iyakar Najeriya da Kamaru, sun ce, mayakan Boko Haram sun kai wasu hare-hare a garin na su cikin dare zuwa safiyar Litinin.
Wani mazaunin garin da harin ya rutsa da shi ya shaidawa BBC cewa, sun ji karar harbe-harbe a wajen garin da tsakar dare, kuma daga baya sai suka ji karar wasu abubuwa masu fashewa.
Ya ce, “Abin da ya faru shi ne jiya wajen karfe 12 da minti 5, mun ji karar harbin bindiga ko’ina cikin garin Gamboru-Ngala kusa da makarantar firamare da ake kira Central Primary School. Akwai wani sansanin jami’an tsaro haka a cikin makarantar.”
Ya ce kuma ce baya ga harbe-harben, maharan sun harba rokoki cikin makarantar.