fidelitybank

Mayakan Boko Haram da ISWAP sun mika wuya

Date:

‘Yan Boko Haram da na ƙungiyar Iswap 47 ne suka muƙa wuya ga sojojin haɗin gwiwa da ke yaƙi da Boko Haram a ƙasashen yankin Tafkin Chadi.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, ya ce mutanen da suka haɗa da maza bakwai da mata 9 da ƙananan yara 31, sun miƙa kansu ne a garin Kwatan Turare da ke Doron Baga a ƙaramar hukumar Kukawa na jihar Borno.

Sojojin sun ce binciken farko ya nuna cewa, mutanen sun tsere ne daga wani gari da ake kira Sharama da ke tsakiyar tsibirin Tafkin Chadi.

Daga cikin mutanen da suka miƙa wuya akwai, Mallam Muazu Adamu wani fitaccen mayaƙin ƙungiyar Boko Haram ɓangaren Shekau, da ya yi aiki ƙarƙashin kwamanda Alai Gana.

Mutanen sun shaida wa sojojin cewa suna gudanar da sana’ar noma a garin da suke kafin su yanke shawarar miƙa kansu.

Mallam Muazu Adamu ya miƙa kansa ga sojojin tare da iyalansa

Sojojin sun ce suna zurfafa bincike kan mutanen domin samun wasu ƙarin bayanai daga gare su.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp