fidelitybank

Mayakan Boko Haram 46 sun tuba a Chadi

Date:

Rundunar dakarun ƙasashen da ke yaƙi da ƙungiyar Boko Haram ta MNJTF ta samu nasarar karɓar tubabbun mayaƙan ƙungiyar su 46 tare da hannunta su ga hukumomin Chadi.

Babban kwamandan rundunar shiyya ta biyu Manjo Janar Djouma Youssouf Mahamat Itno, ne ya jagoranci miƙa tubabbn mayaƙan ga ƙasar Chadi.

An miƙa tsoffin mayaƙan ne a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da aka gudanar a Bagasola na ƙasar Chadi.

Ministan ayyukan gwamnatin ƙasar da kyautata zamantakewa na ƙasar Abdoulaye Mbodou Mbami ya ƙarbi tsofinmayaƙa a madadin gamnatin ƙasar.

Wannan wani ɓangaren na yunƙurin rundunar MNJTF da hukumomin ƙasashen da ke fama da matsalar Boko Haram, na ganin cewa mayaƙan ƙungiyar sun ajiye makamai tare da komawa cikin al’umma domin ci gaba da rayuwa.

Kungiyar Boko Haram dai ta shafe shekaru masu yawa tana kai hare-hare a ƙasashen yankin tafkin Chadi, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane, tare da raba miliyoyi da muhallansu.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp