Aƙalla mayaƙa 20 da ake kyautata zaton ƴan Boko Haram ne aka kashe a Kudancin Nijar a wani farmaki da dakarun haɗin guiwa suka kai.
Jaridar ActuNiger ta rawaito cewa, sanarwa daga rundunar dakarun haɗin guiwa ta MNJTF ta ce, sojojin sun kai farmaki ne tsakanin ranakun 12 zuwa 15 ga Fabrairu bayan hare-haren Boko Haram sun yi ƙamari a yankin rafin kogin Komadougou na Yobe da ke kan iyakar Nijar da Najeriya.
Rundunar ta ce, sojojinta na ƙasa tare da taimakon na sama sun tarwatsa ƴan Boko Haram a ƙauyukan Bague da Kiassa da Digaya da Boulayi da Boulagana da Jabulam da Abadam.
ActuNiger ta kuma ce, akalla mutum 20 yawancinsu mata aka sace, tun a farko Fabrairu a yankin da ke kan iyaka da jihar Borno mai dama da hare-haren Boko Haram.