Rahotanni sun bayyana cewa, wasu da ake zargin mayakan da ke biyayya ga wata kungiya mai suna Biafra Nations League, BNL, sun harbe wasu masu rakiyar wani jirgin ruwa a kusa da ruwan kasar Kamaru.
Lamarin dai a cewar shaidun gani da ido, ya faru ne da misalin karfe 4 na safe a yankin Idabato na yankin Bakassi, yankin da Kamaru ke iko da shi.
Shaidu sun ce mayakan sun kuma kai hari kan jirgin wanda ba ya tafiya kuma ba a tabbatar da asalin sa ba.
“Sun yi yunkurin bankawa jirgin ruwan wuta”, wata majiya ta bayyana.
Ya ce mayakan sun tsere ne kafin isowar sojojin Kamaru.
A cikin wata sanarwa, shugaban BnL, Princewill Richards ya ba da sanarwar dakatar da jiragen ruwa da ke karbar mai a gabashin gabar tekun Guinea.
Ya yi gargadin cewa tasoshin mai suna jefa rayuwarsu cikin hadari.