Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe wasu manoma 23 da kuma masunta a wani hari da ta kai ƙauyen Malam Karanti kusa da Baga a karamar hukumar Kukawa na jihar Borno.
Majiyoyi sun ce mayaƙan sun tara manoman da kuma masunta ne wuri ɗaya, inda suka kashe manoman wake 23.
An hana mazauna garin ɗaukar gawawwakin ƴan uwansu da aka kashe, kamar yadda gidan talabijin na Channels a Najeriya ya ruwaito.
“Mun yi ƙoƙarin zuwa don ɗaukar gawawwakin waɗanda aka kashe tare da jami’an tsaro, sai dai mayaƙan sun hana mu yin haka. Iyalai da dama na jiran gawawwakin ƴan uwansu,” in ji wani ɗan garin.
Ƙauyen Malam Karanti matattara ne na mayaƙan ISWAP, wuri kuma da fararen hula ke noma da kamun kifi duk da irin barazanar da suke fuskanta.