fidelitybank

Max Air ya magantu bayan jirgi ya yi hatsari a Kano

Date:

Kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Max Air ya tabbatar a hukumance cewa ɗaya daga cikin jiragensa ya yi hatsari a lokacin da ya zo sauka a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano da yammacin ranar Talata.

Wannan lamarin ya faru ne da misalin karfe 10:57 na dare, bayan da jirgin da ya taso daga Legas ya sami tangarɗa a tayoyinsa na gaba a lokacin da ya ke shirin sauka.

Ba a dai samu rahoton rasa rai ko jikkata a hatsarin ba.

“Muna so mu sanar da jama’a cewa ɗaya daga cikin jiragenmu ya samu matsala yayin da ya ke ƙoƙarin sauka a Kano da yammacin jiya,” in ji Max Air a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba.

Kamfanin ya ce titin saukan jirgi na filin jirgin saman Kano zai ci gaba da zama a rufe na wani ɗan lokaci yayin da ake tabbatar da cewa an kawar da duk tarkace, wanda hakan na iya haifar da tsaiko a ayyukan sufurin jirgi a ranar Laraba.

Ya yanzu dai hukumar binciken hatsarin jiragen sama ta Najeriya (NSIB) ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.

Wannan dai shi ne karo na biyu cikin wata guda da jirgin kamfanin Max Air zai yi saukar gaggawa a ƙasar.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...
X whatsapp