Kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Max Air ya tabbatar a hukumance cewa ɗaya daga cikin jiragensa ya yi hatsari a lokacin da ya zo sauka a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano da yammacin ranar Talata.
Wannan lamarin ya faru ne da misalin karfe 10:57 na dare, bayan da jirgin da ya taso daga Legas ya sami tangarɗa a tayoyinsa na gaba a lokacin da ya ke shirin sauka.
Ba a dai samu rahoton rasa rai ko jikkata a hatsarin ba.
“Muna so mu sanar da jama’a cewa ɗaya daga cikin jiragenmu ya samu matsala yayin da ya ke ƙoƙarin sauka a Kano da yammacin jiya,” in ji Max Air a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba.
Kamfanin ya ce titin saukan jirgi na filin jirgin saman Kano zai ci gaba da zama a rufe na wani ɗan lokaci yayin da ake tabbatar da cewa an kawar da duk tarkace, wanda hakan na iya haifar da tsaiko a ayyukan sufurin jirgi a ranar Laraba.
Ya yanzu dai hukumar binciken hatsarin jiragen sama ta Najeriya (NSIB) ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.
Wannan dai shi ne karo na biyu cikin wata guda da jirgin kamfanin Max Air zai yi saukar gaggawa a ƙasar.