fidelitybank

Max Air ya magantu bayan jirgi ya yi hatsari a Kano

Date:

Kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Max Air ya tabbatar a hukumance cewa ɗaya daga cikin jiragensa ya yi hatsari a lokacin da ya zo sauka a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano da yammacin ranar Talata.

Wannan lamarin ya faru ne da misalin karfe 10:57 na dare, bayan da jirgin da ya taso daga Legas ya sami tangarɗa a tayoyinsa na gaba a lokacin da ya ke shirin sauka.

Ba a dai samu rahoton rasa rai ko jikkata a hatsarin ba.

“Muna so mu sanar da jama’a cewa ɗaya daga cikin jiragenmu ya samu matsala yayin da ya ke ƙoƙarin sauka a Kano da yammacin jiya,” in ji Max Air a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Laraba.

Kamfanin ya ce titin saukan jirgi na filin jirgin saman Kano zai ci gaba da zama a rufe na wani ɗan lokaci yayin da ake tabbatar da cewa an kawar da duk tarkace, wanda hakan na iya haifar da tsaiko a ayyukan sufurin jirgi a ranar Laraba.

Ya yanzu dai hukumar binciken hatsarin jiragen sama ta Najeriya (NSIB) ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.

Wannan dai shi ne karo na biyu cikin wata guda da jirgin kamfanin Max Air zai yi saukar gaggawa a ƙasar.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp