fidelitybank

Mawaƙa ku taru ku waƙe Najeriya – Ministar Fasaha

Date:

Ministar fasaha da harkokin ƙirƙire-ƙirƙire, Hannatu Musa  Musawa, ta buƙaci marubutan waƙoƙi da mawaƙa daga ko’ina cikin Najeriya su samar da wata waƙa ta musamman ga ƙasa.

Ta ce tana ganin yana da mahimmanci a sami waƙar da ke wakiltar ƙasar gaba ɗaya.

Ministar ta kara da cewa waƙar, wadda za ta zama sabon kirarin ƙasar, za ta taimaka wa mutane su ƙara yin imani da Najeriya da manufofinta

A cewar wata sanarwa da ofishin yada labarai na ministar ya fitar a ranar Talata, ta bayyana hakan ne jim kadan bayan naɗa ta a kan muƙamin.

“A gaskiya ina son mu samu wani sabon take na musamman da ke wakiltar Najeriya, ina fata marubuta waka da masu kade-kade daga sassa daban-daban na kasar nan za su fara tunanin hakan.” in ji sanarwar

Hannatu Musawa ta kuma yi alkawarin yin aiki tukuru domin ganin martabar Najeriya ta inganta.

Ta ce bai kamata a san Najeriya da munanan abubuwa kamar talauci da zamba da ta’addanci ba.

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp