fidelitybank

Matsin rayuwa: Mahaifi ya yi yunƙurin sayar da ƴaƴansa mata 2 a Akwa Ibom

Date:

Rundunar Tsaro ta ‘Civil Defence’ a Akwa Ibom ta ce ta samu nasarar kama wani mahaifi, Elisha Effiong ɗan shekara 40 yayin da ya ke yunƙurin sayar da ƴaƴansa mata guda biyu a kan kuɗi naira 700,000.

Kakakin rundunar, Ukeme Umana ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a birnin Uyo a jiya Laraba.

Ya ce an cafke mai laifin ne a wani asibiti mai suna Full Care Hospital da ke kan titin Ekpanya a nan Uyo ɗin bayan da wani mai gadi ya tseguntawa rundunar.

Umana ya ƙara da cewa an cafke mahaifin ne a ranar 15 ga watan Nuwamba a daidai ƙarfe 1:15 tare da ƴaƴan nasa Abasifreke Edet ƴar shekara 6 da kuma Rachael Edet, mai shekara 4.

Kakakin ya ƙara da cewa da mahaifin ya shiga hannu, ya faɗawa jami’an tsaro cewa shi a zaune ya ke Adidikim da ke Ƙasar Kamaru.

“Ya kuma baiyana mana cewa wai talauci ne da matsin rayuwa ya sanya shi da matarsa da take can Adidikim ɗin su ka yanke shawarar sayar da yaran,” in ji Umana.

Umana ya ƙara da cewa an kammala binciken farko, inda rundunar za ta mayar da maganar zuwa Hukumar Yaƙi da Fataucin Ɗan’adam domin ta kai shi kotu.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp