fidelitybank

Matsin rayuwa: Mahaifi ya yi yunƙurin sayar da ƴaƴansa mata 2 a Akwa Ibom

Date:

Rundunar Tsaro ta ‘Civil Defence’ a Akwa Ibom ta ce ta samu nasarar kama wani mahaifi, Elisha Effiong ɗan shekara 40 yayin da ya ke yunƙurin sayar da ƴaƴansa mata guda biyu a kan kuɗi naira 700,000.

Kakakin rundunar, Ukeme Umana ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a birnin Uyo a jiya Laraba.

Ya ce an cafke mai laifin ne a wani asibiti mai suna Full Care Hospital da ke kan titin Ekpanya a nan Uyo ɗin bayan da wani mai gadi ya tseguntawa rundunar.

Umana ya ƙara da cewa an cafke mahaifin ne a ranar 15 ga watan Nuwamba a daidai ƙarfe 1:15 tare da ƴaƴan nasa Abasifreke Edet ƴar shekara 6 da kuma Rachael Edet, mai shekara 4.

Kakakin ya ƙara da cewa da mahaifin ya shiga hannu, ya faɗawa jami’an tsaro cewa shi a zaune ya ke Adidikim da ke Ƙasar Kamaru.

“Ya kuma baiyana mana cewa wai talauci ne da matsin rayuwa ya sanya shi da matarsa da take can Adidikim ɗin su ka yanke shawarar sayar da yaran,” in ji Umana.

Umana ya ƙara da cewa an kammala binciken farko, inda rundunar za ta mayar da maganar zuwa Hukumar Yaƙi da Fataucin Ɗan’adam domin ta kai shi kotu.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp