fidelitybank

Matsalar tsaro ne ya sanya mu ka ƙasa gama gyaran wutar Arewa – TCN

Date:

Kamfanin rarraba wutar lantarki na ƙasa TCN, ya bayyana cewa aikin gyara layin samar da lantarki na Apir-Ugaji ya ɗauki tsawon lokaci ba a kammala ba ne saboda matsalar tsaro a yankin.

Da yake magana a wani taron manema labarai a yau Talata, Manajan Darektan, kamfanin Injiniya Abdulaziz Sule, ya ce injiniyoyin da ke gyaran suna aiki ne bisa kulawar jami’an tsaro -sojoji, kuma da zarar ƙarfe 6 na yamma ya yi dole ne su bar wajen su je wajen da babu matsalar tsaro su kwana sannan da safe su koma bakin aiki.

Amma duk da haka ya ce, za a kammala aikin a cikin kwana biyu ko uku a hanyar wadda take da wani layin na samar da lantarki ga Kano da sauran manyan birane a arewacin Najeriya.

Shugaban ya kuma ce shi ma layin na biyu wanda aka lalata wajen turakuna biyar nasa zai dawo bakin aiki aƙalla zuwa ranar Lahadi – cikin kwana biyar kenan.

Injiniya Sule ya ƙara da cewa da zarar an kammala gyaran layukan biyu, za a iya aikawa da wutar lantarkin da aƙalla ta kai yawan megawatt 500 zuwa 600 ga yankin arewacin Najeriyar.

A kan abin da kamfanin yake yi kuma don hana ɓarnata kayan samar da wutar lantarkin, ya ce suna haɗa kai da al’ummomin yankunan, inda har ma suna ba su kuɗin sufuri da kuma waya don sheda msu duk wani abu da suka gani da zai yi illa ga layukan samar da wutar.

Sannan ya ce suna kuma haɗa kai da jami’an tsaro – sojoji da ‘yansanda da rundunar tsaro da kai ɗauki (Civil_Defense…), domin tabbatar da ganin suna sintiri a wuraren kayan samar da lantarkin

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp