fidelitybank

Matsalar tsaro ne ya sanya mu ka ƙasa gama gyaran wutar Arewa – TCN

Date:

Kamfanin rarraba wutar lantarki na ƙasa TCN, ya bayyana cewa aikin gyara layin samar da lantarki na Apir-Ugaji ya ɗauki tsawon lokaci ba a kammala ba ne saboda matsalar tsaro a yankin.

Da yake magana a wani taron manema labarai a yau Talata, Manajan Darektan, kamfanin Injiniya Abdulaziz Sule, ya ce injiniyoyin da ke gyaran suna aiki ne bisa kulawar jami’an tsaro -sojoji, kuma da zarar ƙarfe 6 na yamma ya yi dole ne su bar wajen su je wajen da babu matsalar tsaro su kwana sannan da safe su koma bakin aiki.

Amma duk da haka ya ce, za a kammala aikin a cikin kwana biyu ko uku a hanyar wadda take da wani layin na samar da lantarki ga Kano da sauran manyan birane a arewacin Najeriya.

Shugaban ya kuma ce shi ma layin na biyu wanda aka lalata wajen turakuna biyar nasa zai dawo bakin aiki aƙalla zuwa ranar Lahadi – cikin kwana biyar kenan.

Injiniya Sule ya ƙara da cewa da zarar an kammala gyaran layukan biyu, za a iya aikawa da wutar lantarkin da aƙalla ta kai yawan megawatt 500 zuwa 600 ga yankin arewacin Najeriyar.

A kan abin da kamfanin yake yi kuma don hana ɓarnata kayan samar da wutar lantarkin, ya ce suna haɗa kai da al’ummomin yankunan, inda har ma suna ba su kuɗin sufuri da kuma waya don sheda msu duk wani abu da suka gani da zai yi illa ga layukan samar da wutar.

Sannan ya ce suna kuma haɗa kai da jami’an tsaro – sojoji da ‘yansanda da rundunar tsaro da kai ɗauki (Civil_Defense…), domin tabbatar da ganin suna sintiri a wuraren kayan samar da lantarkin

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp