fidelitybank

Matsalar sabon kudi da man fetur zai kawo cikas a zaben Najeriya – Bankin Duniya

Date:

Ofishin Bankin Duniya da ke Najeriya, ya yi gargaɗin cewa matsalar ƙarancin man fetur da na sabbin takardun kuɗin ƙasar ka iya kawo rashin tabbas game da yiyuwar babban zaɓen ƙasar da ke tafe cikin wannan wata.

Bankin Duniyar ya ce wa’adin da Babban Bankin ƙasar ya saka na daina amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar zai shafi harkokin zamantakewa da kasuwancin al’ummar ƙasar.

Bayanan da bankin Duniyar ya wallafa a shafinsa na internet na cewa “Sakamakon ƙarancin sabbin takardun kuɗi da man fetur wanda aka shafe watanni ana fama da shi a ƙasar. Akwai yiyuwar ‘yan ƙasar su faɗa cikin wahalhalu da matsai, lamarin da zai iya tayar da hankula har ma ya shafi babban zaɓen ƙasar da ke tafe cikin watannin fabrairu da Maris”

Bankin ya ƙara da cewa kashi 45 na matasan ƙasar ne ke da asusun ajiya na banki, kuma kashi 34 cikin ɗari ne ke hada-hadar kuɗi ta internet.

Tun da farko dai Babban Bankin ƙasar ya saka 31 ga watan Janairu a matsayin wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar.

To sai dai bayan shan kiraye-kiraye gwamnan Babban Bankin ƙasar ya nemi amincewar shugaban ƙasar domin ƙara wa’adin zuwa 10 ga watan Fabrairu.

To sai dai tun bayan ƙara wa’adin babu abin da ya sauya na ƙarancin kuɗin inda miliyoyin ‘yan ƙasar ke fama da bin dogayen layuka wajen cirar kuɗi kama daga bankuna zuwa na’u’rorin cirar kuɗi na ATM da wajajen masu POS.

Yayin da ‘yan siyasa ke ci gaba da ɗora laifin kan juna, Babban Bankin ƙasar na zargin bankunan ƙasar da ɓoye maƙudan sabbin takardun kuɗin.

Masana dai na ganin cewar bayanan da Bankin Duniyar ya fitar a shafinsa na Internet abu ne da ya kamata a lura da shi, domin kuwa ‘yan ƙasar da dama na ci gaba da fuskantar wahalhalu wajen samun kudin da za su ciyar da iyalansu.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp