fidelitybank

Matsalar sabon kudi da man fetur zai kawo cikas a zaben Najeriya – Bankin Duniya

Date:

Ofishin Bankin Duniya da ke Najeriya, ya yi gargaɗin cewa matsalar ƙarancin man fetur da na sabbin takardun kuɗin ƙasar ka iya kawo rashin tabbas game da yiyuwar babban zaɓen ƙasar da ke tafe cikin wannan wata.

Bankin Duniyar ya ce wa’adin da Babban Bankin ƙasar ya saka na daina amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar zai shafi harkokin zamantakewa da kasuwancin al’ummar ƙasar.

Bayanan da bankin Duniyar ya wallafa a shafinsa na internet na cewa “Sakamakon ƙarancin sabbin takardun kuɗi da man fetur wanda aka shafe watanni ana fama da shi a ƙasar. Akwai yiyuwar ‘yan ƙasar su faɗa cikin wahalhalu da matsai, lamarin da zai iya tayar da hankula har ma ya shafi babban zaɓen ƙasar da ke tafe cikin watannin fabrairu da Maris”

Bankin ya ƙara da cewa kashi 45 na matasan ƙasar ne ke da asusun ajiya na banki, kuma kashi 34 cikin ɗari ne ke hada-hadar kuɗi ta internet.

Tun da farko dai Babban Bankin ƙasar ya saka 31 ga watan Janairu a matsayin wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar.

To sai dai bayan shan kiraye-kiraye gwamnan Babban Bankin ƙasar ya nemi amincewar shugaban ƙasar domin ƙara wa’adin zuwa 10 ga watan Fabrairu.

To sai dai tun bayan ƙara wa’adin babu abin da ya sauya na ƙarancin kuɗin inda miliyoyin ‘yan ƙasar ke fama da bin dogayen layuka wajen cirar kuɗi kama daga bankuna zuwa na’u’rorin cirar kuɗi na ATM da wajajen masu POS.

Yayin da ‘yan siyasa ke ci gaba da ɗora laifin kan juna, Babban Bankin ƙasar na zargin bankunan ƙasar da ɓoye maƙudan sabbin takardun kuɗin.

Masana dai na ganin cewar bayanan da Bankin Duniyar ya fitar a shafinsa na Internet abu ne da ya kamata a lura da shi, domin kuwa ‘yan ƙasar da dama na ci gaba da fuskantar wahalhalu wajen samun kudin da za su ciyar da iyalansu.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp