fidelitybank

Matsalar sabon kudi da man fetur zai kawo cikas a zaben Najeriya – Bankin Duniya

Date:

Ofishin Bankin Duniya da ke Najeriya, ya yi gargaɗin cewa matsalar ƙarancin man fetur da na sabbin takardun kuɗin ƙasar ka iya kawo rashin tabbas game da yiyuwar babban zaɓen ƙasar da ke tafe cikin wannan wata.

Bankin Duniyar ya ce wa’adin da Babban Bankin ƙasar ya saka na daina amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar zai shafi harkokin zamantakewa da kasuwancin al’ummar ƙasar.

Bayanan da bankin Duniyar ya wallafa a shafinsa na internet na cewa “Sakamakon ƙarancin sabbin takardun kuɗi da man fetur wanda aka shafe watanni ana fama da shi a ƙasar. Akwai yiyuwar ‘yan ƙasar su faɗa cikin wahalhalu da matsai, lamarin da zai iya tayar da hankula har ma ya shafi babban zaɓen ƙasar da ke tafe cikin watannin fabrairu da Maris”

Bankin ya ƙara da cewa kashi 45 na matasan ƙasar ne ke da asusun ajiya na banki, kuma kashi 34 cikin ɗari ne ke hada-hadar kuɗi ta internet.

Tun da farko dai Babban Bankin ƙasar ya saka 31 ga watan Janairu a matsayin wa’adin amfani da tsoffin takardun kuɗin ƙasar.

To sai dai bayan shan kiraye-kiraye gwamnan Babban Bankin ƙasar ya nemi amincewar shugaban ƙasar domin ƙara wa’adin zuwa 10 ga watan Fabrairu.

To sai dai tun bayan ƙara wa’adin babu abin da ya sauya na ƙarancin kuɗin inda miliyoyin ‘yan ƙasar ke fama da bin dogayen layuka wajen cirar kuɗi kama daga bankuna zuwa na’u’rorin cirar kuɗi na ATM da wajajen masu POS.

Yayin da ‘yan siyasa ke ci gaba da ɗora laifin kan juna, Babban Bankin ƙasar na zargin bankunan ƙasar da ɓoye maƙudan sabbin takardun kuɗin.

Masana dai na ganin cewar bayanan da Bankin Duniyar ya fitar a shafinsa na Internet abu ne da ya kamata a lura da shi, domin kuwa ‘yan ƙasar da dama na ci gaba da fuskantar wahalhalu wajen samun kudin da za su ciyar da iyalansu.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp