Zanga-zanga ta ɓarke a Abeukuta babban birnin jihar Ogun ranar Talata, sakamakon matsalar ƙarancin kuɗi da ke ci gaba ci wa al’ummar ƙasar tuwo a ƙwarya.
Masu zanga-zangar sun mamaye unguwannin Aladesanmi da Fajol da Somorin a yankin Obantoko da ke Abeokuta inda suka riƙa cinna wuta tare da rera waƙoƙin adawa da CBN.
Rahotonni sun ce an lalata reshen bankin First Bank da ke Sapon, a yayin da masu zanga-zangar suka yi yunƙurin cinna masa wuta.
Karanta Wannan:
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Abimbola Oyeyemi ya ce an kai jami’an tsaro wajen domin sanya idanu da kare ɓarna da asarar rayuka da dukiyoyi.
Haka kuma can ma a maƙwanciyar jihar Ondo rahotonni sun ce wasu mutane sun ɓarke da zanga-zanga domin nuna damuwarsu kan ƙarancin man fetur da sabbin takardun kuɗi.
Masu zanga-zangar sun hana ababen hawa da da jama’a bin babbar hanyar Ore zuwa Benin da ke jihar.
Jami’an ‘yan sandan jihar sun buƙaci mutane da kada su shiga zanga-zangar.