Dan takarar shugaban kasa a jamâiyyar All Progressives Congress, APC, Bola Tinubu, ya ce, Bishop Matthew Kukah na darikar Katolika na Sokoto ya girme shi da watanni kadan.
Tinubu ya yi magana ne a yayin bikin cika shekaru 70 na Bishop Kukah a jiya.
Ya yabawa Kukah bisa kyawawan ayyuka, yana mai jaddada cewa ya fahimci abin da malamin yake ginawa.
Tinubu ya ce dukkansu suna da babban nauyi a wuyansu wajen gina Najeriya.
A cewar Tinubu: âKuna gina wata cibiya don girmama ku 70, ni 70 kuma har yanzu zan iya ba da gudummawa. Na girme ka watanni kacal.
âAmma Bishop, za ka taimaka wajen gina Najeriya. Girman al’umma yana kan kafadar ku. Yana kan kafada na kuma, kuma dole ne mu gina shi tare.
“Dole ne, kuma zan ba da gudummawa mai kyau da kuma ni kaina don ginawa da ganin kammala wannan cibiyar.”
A tsawon shekaru, an yi ta cece-kuce kan shekarun Tinubu.
Yayin da wasu âyan Najeriya ke ganin cewa Tinubu ya haura shekaru 80, dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar APC ya dage cewa shekarunsa 70 ne.