Domin yakar ‘yan ta’addan da suka yi tashe-tashen hankula a Jihar Zamfara yadda ya kamata, Gwamna Bello Mohammed Matawalle, ya fara horas da sabbin jami’an kare al’umma.
Gwamnan ya bada tabbacin cewa gwamnatin sa ta bullo da matakan da suka dace na yaki da tada kayar bayan da suka kawo cikas ga ci gaban jihar.
Ya ce, an dauki jami’an kare hakkin jama’a ne daga kowace masarautu 19 na jihar.
Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da tuta na horas da masu gadi a Gusau, Matawalle ya ce, gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da sabbin matakan tsaro da za su dakile tabarbarewar tsaro a kowane bangare na jihar.
Gwamnan ya ce, an yanke shawarar kafa jami’an kare hakkin jama’a ne saboda burin gwamnatinsa na samar da duk hanyoyin da za a bi domin magance yawaitar ayyukan ‘yan fashi da ke haddasa asarar rayuka, wahalhalun da ba a taba gani ba da kuma wargaza zaman lafiya a wasu sassan jihar. .
Ya bukaci sabbin masu gadin da aka dauka da su mayar da hankali sosai kan horar da su da kuma aikin tabbatar da tsafta a jihar.
Gwamna Matawalle ya bayyana cewa, a matsayinsu na masu kare al’umma, nasu kira ne na kishin kasa, sunayensu zai yi fice a tarihi a matsayin mutane masu kishin kasa, rashin son kai da son zaman lafiya.